News
Zaɓen fidda gwani a Ekiti: Ƴan APC sun yi bore
Daga Yasir sani Abdullah
Ƴan jam’iyyar APC a Jihar Ekiti sun gudanar da zanga-zangar adawa da yadda zaben fidda gwani na gwamna ya ke gudana a jihar.
A yau Alhamis ne a ka shirya gudanar da zaɓen.
Ƴan jam’iyar da su ka hallara a sakatariyar jam’iyyar su na zargin gwamnatin jihar, ƙarƙashin APC da rashin adalci a cikin wannan tsari.
Duk da cewa an fara tantancewa a wasu unguwanni, ƴan jam’iyyar da suka yi zanga-zanga a sakatariyar sun ce ba za su shiga cikin zaben ba.
ya’yan jam’iyyar sun yi ta ihu su na cewa “Ba zaɓe! Ba a zaɓen fidda gwani a Ekiti,” ‘
Wannan lamari dai na zuwa ne bayan Sanata kuma daya daga cikin masu neman takarar, Sanata Opeyemi Bamidele ya bukaci jam’iyyar APC da ta dakatar da yin zaɓen na fidda gwani a jihar.
-
News3 days agoWasu Ƴan Daba Sun Kai Farmaki Kasuwar Siyar Da Wayoyi Ta Farm Center Dake Kano
-
News5 days agoWasu Fusatattun Matasa Sun Ƙona Mutum Uku Har lahira A Filato
-
News5 days agoAbin Takaici Ne A Kyale Mata Su Cire Wandunan Da Aka Basu Akan Titi Suna Dagawa A Cikin Al’ummar Da Ke Alfahari Da Kunya Da Addini
