News
Gwamnatin Kano ta fara shirye-shiryen ƙara shekarun ritayar malaman makaranta
Daga kabiru basiru fulatan
Gwamnatin Jihar Kano ta kafa wani kwamiti da zai yi garambawul na tsari da yanayin aikin malaman makaranta a jihar.
Kwamishinan Yaɗa Labarai na jihar, Muhammad Garba ne ya baiyana haka a wata sanarwa da ya fitar a jiya Asabar.
A sanarwar, Garba ya ce batun na ɗaya da ga cikin ƙudurirorin taron majalisar zartsawa.
Ya ce kwamitin zai zana jadawalin yin ritayar malamai na bai-ɗaya, wanda zai fara aiki da ga watan Janairun da ya gabata.
An umarci kwamitin, in ji Garba, da ya samar da wani tsari mai kyau da zai samar da nasarar sabon tsarin.
Kwamishinan ya ce sabuwar shekarun ritaya zai kasance da ga 35 zuwa 40 da kuma shekara 60 zuwa 64 na haihuwa.
-
News3 days agoWasu Ƴan Daba Sun Kai Farmaki Kasuwar Siyar Da Wayoyi Ta Farm Center Dake Kano
-
News6 days agoWasu Fusatattun Matasa Sun Ƙona Mutum Uku Har lahira A Filato
-
News5 days agoAbin Takaici Ne A Kyale Mata Su Cire Wandunan Da Aka Basu Akan Titi Suna Dagawa A Cikin Al’ummar Da Ke Alfahari Da Kunya Da Addini
