News
Duk lalacewar PDP gwara ita da APC, innji Kwankwaso
Daga yasir sani abdullahi
Tsohon gwamnan Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya ce jam’iyyar APC ce mafi lalacewa cikin jam’iyyun siyasa a wannan lokaci.
Tsohon Sanatan ya kuma ce dukda dai itama PDP ɗin ba kanwar lasa bace wajen kama-karya a yanzu, amma dai za a iya cewa gwara-gwara idan a ka kwatanta ta da APC.
Kwankwaso ya yi wannan furuci ne a jiya Lahadi, yayin taron masu ruwa da tsaki na ɗarikar Kwankwasiyya a gidansa dake Kano.
Ya ce wasu “sojojin gona” ne su ke yin kama-karya a PDP, inda ya koka da cewa duk cancantar mutum da haƙƙin sa, zai iya rasa shi ta dalilin waɗannan sojojin gonar.
Kwankwaso ya jadda cewa har yanzu yana cikin jam’iyyar PDP, amma shirye-shirye sunyi nisa a tsakaninsa da jam’iyyar NNPP.
Kwankwaso yace fita daga jam’iyya da komawa ba illa bane, kuma hakan ma shi ne kwarewa a siyasa.
Ya tuna cewa a shekarar 2018 da su ka yi zaben fidda gwani a Fatakwal, wadanda su ka zo na farko, na biyu, na uku da na hudu, duk sunbar PDP sun dawo, “sai kuma wasu tarkace da suka biyo baya, a cewar Kwankwaso.”
-
News3 days agoWasu Ƴan Daba Sun Kai Farmaki Kasuwar Siyar Da Wayoyi Ta Farm Center Dake Kano
-
News6 days agoWasu Fusatattun Matasa Sun Ƙona Mutum Uku Har lahira A Filato
-
News5 days agoAbin Takaici Ne A Kyale Mata Su Cire Wandunan Da Aka Basu Akan Titi Suna Dagawa A Cikin Al’ummar Da Ke Alfahari Da Kunya Da Addini
