News
Sarkin Zazzau ya dakatar da hakimai 4
Daga kabiru basiru fulatan
Mai martaba Sarkin Zazzau Malam Ahmad Nuhu Bamalli, ya dakatar da wasu hakimansa 4, jim kadan bayan sauka daga hawan Idi, sakamakon karya dokokin hawan Daba na masarautar.
Wannan na zuwa ne ta cikin wata sanarwa da jami’in yada labaran masarautar, Abdullahi Aliyu Kwarbai, ya fitar, inda yace dakatarwar ta fara aiki ne nan take.
A cewar sanarwar hakiman da aka dakatar sun hadar Uban Garin Zazzau kuma hakimin Soba Alhaji Bashir Shehu Idris, da Sarkin Dajin Zazzau kuma hakimin Kubau Alhaji Shehu Umar Aliyu.
Sauran sun hadar da wakilin Birnin Zazzau Alhaji Suleiman Ibrahim Dabo da kuma Garkuwan kudun Zazzau Alhaji Muhammad Sani Uwais.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
