News
Shugaba Buhari Ga Najeriya: Ba Zan Huta Ba Har Sai An Samu Zaman Lafiya a Kasar Nan.
Daga Muhammad Muhammad zahraddin
Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ce gwamnatinsa ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen kokarin dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a kasar nan.
Buhari ya bayyana haka ne yayin bikin cika shekaru 58 da kafa rundunar sojojin saman Najeriya a nan Kano.
Shugaban ya ce zuba jarin da gwamnatinsa ta yi a rundunar sojin sama ya taimaka wajen karya lagwon ‘yan ta’adda a kasar nan.
Ya yi alkawarin cewa, zai ci gaba da bai wa sojin sama goyon baya da ya dace a yaki da rashin tsaro da kasar nan ke fuskanta.
Ya kuma ce gwamnatin sa baza ta gushe ba, har sai ta samar da ingantaccen tsaro a fadin kasar nan.
Kazalika Shugaba Muhammadu Buhari ya sadu da iyalan da suka rasa rayukansu sakamakon fashewar da aka samu a unguwar Sabon Gari a makon da ya gabata.
Shugaban ya jajanta wa iyalan mutanen da wannan hatsari ya rutsa da su da Mai Martaba Sarkin Kano da kuma gwamna kan wannan lamari.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
