News
Sagagi zai cigaba da kasancewa shugaban PDP a Kano har karshen 2024 — Kotu
Daga Hamza Yusuf Abdulmumin
Wata babbar kotun tarayya dake zamanta a babban birnin tarayya Abuja, ta jaddada batunta na hana uwar jam’iyyar PDP ta kasa cire shugaban jam’iyyar na jihar Kano, Shehu Wada Sagagi, daga mukaminsa, har sai ya kare wa’adinsa kamar yadda doka ta tanadar, inda zai sauka a watan Disambar shekarar 2024, kasancewar an zabe shi ne tare da sauran kunshin shugabancinsa a ranar 14 ga watan Disambar shekarar 2020.
Da yake yanke hukunci a yau Laraba, mai shari’a Jostis Taiwo Taiwo, yace kwamitin kolin jam’iyyar PDP ko wani sashi na jam’iyyar, bashi da ikon sauke duk shugaban da aka zaba ta hanyar da aka amince, saboda haka Sagagi da sauran shugabannin ƙananan hukumomi 44 na Kano sune shugabanni har zuwa karewar wa’adinsu.
Sagagi dai na fuskantar shari’a a wannan tsakanin, kasancewar wani tsagin jam’iyyar a jihar Kano na zarginsa da yin aiki da tsohon gwamnan Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, wanda ya koma jam’iyyar NNPP, abinda Sagagin ya musanta.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
