News
Ɗan Sule Lamido ya zama ɗan takarar gwamna na PDP a Jigawa
Daga yasir sani Abdullah
Mustafa Lamido, ɗan tsohon Gwamna Sule Lamido na Jigawa, ya zama dan takarar gwamnan jihar a ƙarƙashin tutar jam’iyyar PDP a zaben 2023.
Kisan Harira: Abin da Buhari ya ce kan kashe mai ciki da ‘ya’yanta hudu a Anambra
Jami’in kula da zaben fidda-gwani Isah Ahmed ne ya bayyana haka lokacin da ya ke sanar sakamakon zaɓen a yau Laraba a Dutse.
Ahmed ya ce Mustafa ya samu ƙuri’u 829 daga cikin ƙuri’u 832 da aka kaɗa, inda ya ƙara da cewa Saleh Shehu, ya zo na biyu ba tare da ya samu ƙuri’a ko ɗaya ba.
Ya taya wanda ya lashe zaɓen da wakilan jam’iyyar da kuma ‘ya’yan jam’iyyar da yadda suka gudanar da zaɓen ba tare da an samu matsala ba.
Shugaban jam’iyyar PDP na jihar, Babandi Ibrahim, ya ce jam’iyyar za ta yi bakin kokarinta wajen ganin ta gabatar da sahihin ɗan takarar kujerar gwamna a jihar, wanda zai taimaka wajen dawo da martabar jihar da aka rasa.
Mustafa ya bayyana farin cikinsa da nasarar da aka samu, yana mai cewa: “Na amince da wannan takara da gaske cikin tawali’u, imani da kuma jajircewa.
Ya bayyana zaɓen a matsayin tarihi.
“Yayin da muka shiga mataki na gaba na yakin neman zabe, ina rokon ku da ku amince da ni, ku yi aiki da ni, ku yi yakin neman zabe tare da ku zabe ni domin mu sake daukaka jihar nan. Kuma
ina mai kira a gare ku da ku fito kwan ku da kwarkwatar ku don zaben PDP.
“Ina kira gare mu da mu guji siyasar rarrabuwar kawuna da rashin hadin kai. Kare martabar shi ne sama da duk wani son rai.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
