News
Mohammed Salah: Ina nan daram a Liverpool
Daga Usman Abdullahi jibirin
Dan kwallon Liverpool, Mohammed Salah ya ce “tabbas” zai ci gaba da kasancewa a kungiyar a kakar wasa mai zuwa amma kuma ya ki bayyana ko zai sabunta yarjejeniyarsa ko kuma a’a.
Yau za a gudanar da zaben fitar da gwani na gwamnoni a APC
Yarjejeniyar Salah da Liverpool za ta kare ne a watan Yunin 2023 abin da ya janyo ake jita-jitar zai bar Anfield.
“Tabbas zan kasance a nan a kakar wasa mai zuwa. Abin da ke gabanmu shi ne lashe gasar Champions”.
Takwaransa dan kasar Senegel, Sadio Mane, ya ce zai bayyana matsayinsa kan ganiyar bayan sun taka leda da Real Madrid a birnin Paris.
Mohamed Salah ya zura kwallo 31 a Liverpool a kakar bana sannan Sadio Mane ya zura 23
Dan kwallon Senegal din ya zura kwallo 120 a cikin wasa 268 da ya buga wa Liverpool kuma kungilarsa da kungiyar za ta kare ne a watan Yunin badi.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
