News
An kashe fararen hula 20 a Arewacin Mali
Daga Kabiru basiru fulatan
An kashe akalla fararen hula 20 a kusa da birnin Gao da ke Arewacin Mali ranar Asabar.
Advertisements
Advertisements
Hukumomi sun zargi mayaka masu ikirarin jihadi, kuma sun ce lamarin akwai tayar da hankali sosai, lura da yadda fararen hula ke ci gaba da tserewa daga yankin saboda hare-hare.
Ko a ranar Lahadi an kashe sojan wanzar da zaman lafiya na Majalisar Dinkin Duniya, bayan taka nakiya a Kidal da ke arewacin kasar.
Advertisements
Majalisar Dinkin Duniya ta damu da yadda rashin tsaro ke dada kamari a yankunan Gao da Menaka.
Advertisements
Advertisements
Advertisements
