News
Kwale-kwale ya nutse da mai ciki da wasu mutum biyar a Bayelsa
Daga Yasir sani abdullahi
Rahotanni daga yankin karamar hukumar Ijaw ta Kudu a jihar Bayelsa da ke Kudancin Najeriya na cewa mutum shida da suka hada da wata mace mai ciki sun nutse a ruwa, bayan da kwale-kwalensu ya kife.
Hatsarin ya faru ne ranar Asabar da rana.
Jaridun cikin gida sun ruwaito cewa yanzu haka masu aikin ceto na kan neman matafiyan, da suka hada da wata mai hidimar kasa da kuma dattijuwa mai shekara 70.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar yan sanda a jihar Bayelsa, SP Asinim Butswat, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya kara da cewa suna jiran karin bayani kan bayanan mutanen da lamarin ya rutsa da su.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
