News
Shugaba Buhari zai tafi Rwanda
Daga kabiru basiru fulatan
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari zai halarci taron shugabannin ƙungiyar Commonwealth ta ƙasashe rainon Ingila da ke gudana a ƙasar Rwanda daga 20 zuwa 26 ga watan Yuni.
.Jam’iyyar NNPP Tayi Allah-Wadai Da Korar Malaman Makaranta Sama Da Dubu Biyu A Jihar Kaduna
Wata sanarwa da fadar shugaban ƙasa ta fitar a yau Laraba ta ce shugaban zai halarci buɗe bikin a hukumance ranar Juma’a.
Taron mai laƙabin CHOGM 2022, zai tattauna kan halin rayuwa da kuma ci gaban al’ummar ƙungiyar fiye da biliyan biyu da ke zaune a ƙasa 54 na nahiyoyin Afirka da Asiya da Amurka da Turai da kuma yankin Pacific.
Ministci da manyan jami’an gwamnatin Najeriya takwas ne za su yi wa Buhari rakiya zuwa Rwanda.
Ana sa ran shugaban zai koma Najeriya ranar Lahadi, 26 ga watan Yuni.
-
News2 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News2 days ago
Zaben 2027: INEC Ta Amince Da Atiku Abubakar, ‘Yan Takarar ADC 470
