Connect with us

Sports

NPFL: Pillars ta doke Dakkada FC a kwantan wasan mako na 31

Published

on

 

Daga Muhammad Muhammad zahraddin

Advertisement

 

Kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars ta yi nasarar doke Dakkada FC da ci 1 mai ban haushi a gasar cin kofin Firimiya ta Najeriya a kwantan wasan mako na 31.

Advertisement

Dan wasan tsakiya na kungiyar ta Kano Pillars Yusuf Bala Maigoro ne ya zura kwallon data bawa Pillars Nasara a minti na 22 da fara wasa.

An dai buga wasan ne a filin wasa na Sani Abacha dake kofar Mata.

Advertisement

Da wannan sakamakon yanzu haka Pillars na matakin ta 15 da maki 42 a teburin gasar ta shekarar 2021/2022.

Kafin wannan wasa dai Pillars na a matsayin ta 19 a gasar Firimiyar ta Najeriya

Advertisement

 

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending