Connect with us

Sports

Afirka Ta Kudu Ta Doke Najeriya

Published

on

Daga Khadija Abdullahi Mahmud

 

Advertisement

 

Tawagar Banyana Banyana ta kasar Afirka ta Kudu ta doke takwararta ta Super Falcons ta Najeriya da ci biyu da daya.

Advertisement

 

A wasan wanda shi ne na farko a Gasar Cin Kofin ta Mata wato WAFCON, Afirka ta Kudun ta fanshe doke ta da Najeriya ta yi a wasan karshe na gasar ta karshe da aka buga a shekarar 2018.

Advertisement

Girgizar kasa ta hallaka mutum 42 a India
Bayan zuwa hutun rabin lokaci babu ci, tawagar Banyana Banyana ta mamayi Super Falcons, inda ta zura mata kwallo biyu a jere a raga.

Jermaine Seoposenwe ce ta fara jefa kwallo a ragar Najeriya a minti 61 da fara wasa, sai minti 68 da fara wasa Hildah Tholakele Magaia ta kara kwallo na biyu.

Advertisement

Sai daga bisani ’yar wasan Najeriya da ke taka leda a kungiyar Atletico Madrid ta Spain, Rasheedat Ajibade ta farke kwallo daya a minti 91 da fara wasa.

Da wannan sakamakon, Najeriya za a iya cewa ta fara kafar hagu a shirinta na kare kambunta na gasar, da kuma kokarinta na lashe gasar karon na goma.

Advertisement

An buga wasan ne a Filin Wasa na Rabat, Babban Birnin Kasar Morocco.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending