Sports
Afirka Ta Kudu Ta Doke Najeriya
Daga Khadija Abdullahi Mahmud
Tawagar Banyana Banyana ta kasar Afirka ta Kudu ta doke takwararta ta Super Falcons ta Najeriya da ci biyu da daya.
A wasan wanda shi ne na farko a Gasar Cin Kofin ta Mata wato WAFCON, Afirka ta Kudun ta fanshe doke ta da Najeriya ta yi a wasan karshe na gasar ta karshe da aka buga a shekarar 2018.
Girgizar kasa ta hallaka mutum 42 a India
Bayan zuwa hutun rabin lokaci babu ci, tawagar Banyana Banyana ta mamayi Super Falcons, inda ta zura mata kwallo biyu a jere a raga.
Jermaine Seoposenwe ce ta fara jefa kwallo a ragar Najeriya a minti 61 da fara wasa, sai minti 68 da fara wasa Hildah Tholakele Magaia ta kara kwallo na biyu.
Sai daga bisani ’yar wasan Najeriya da ke taka leda a kungiyar Atletico Madrid ta Spain, Rasheedat Ajibade ta farke kwallo daya a minti 91 da fara wasa.
Da wannan sakamakon, Najeriya za a iya cewa ta fara kafar hagu a shirinta na kare kambunta na gasar, da kuma kokarinta na lashe gasar karon na goma.
An buga wasan ne a Filin Wasa na Rabat, Babban Birnin Kasar Morocco.
