Sports
PSG ta nada Galtier a matakin sabon kociyanta
Daga kabiru basiru fulatan.
Paris St-Germain ta nada Christophe Galtier a matakin sabon kociyanta, bayan da ta raba gari da Mauricio Pochettino.
Manyan ministocin Birtaniya biyu sun yi murabus .
Galtier ya saka hannu kan yarjejeniyar kaka biyu da za ta karkare a karshen kakar 2024.
A watan jiya kocin ya bar Nice, bayan da ya ja ragamar kungiyar ta lashe Ligue 1 ta kuma yi ta biyu a French Cup.
Mai shekara 55, wanda ya lashe Ligue 1 da Lille a 2021, shi ne na bakwai da zai horar da PSG tun bayan da attajiran Qatar suka karbi ragamar jan kungiyar a 2011.
Galtier daya ne daga kopci biyu da suka hana PSG daukar Ligue 1, bayan Leonardo Jardim na Monaco a 2016-17.
Ya ajiye aikin horar da Lille, bayan daukar Lille 1 a watan Mayun 2021 daga nan ya koma Nice kaka daya, ya taba kocin Saint-Etienne.
Tun bayan wata daya ake sa ran Pochettino, tsohon wanda ya horar da Tottenham, mai shekara 50, zai bar PSG, amma sai yanzu aka tabbatar da tafiyarsa.
Ana sa ran tsohon kociyan Nice, Christophe Galtier ne zai maye gurbin dan kasar Argentina.Pochettino ya bar PSG, bayan da ya ja ragamar kungiyar ta lashe French League na kakar da aka kammala na 10 jumulla, kuma na farko da ya dauka a matakinsa na koci.
Tsohon mai tsaron bayan PSG, ya ja ragamar dukkan wasa a kakar da wuce a lik ba tare da an doke kungiyar ba a gida, wanda ya yi nasara a wasa 16 daga 19.
PSG ta samu damar lashe babban kofin gasar Faransa, amma an yi waje da ita a zagayen kungiyoyi 16 a Champions League, kofin da Real Madrid ta dauka..
