News
An kawo ƙarshen yunƙurin haɗewa tsakanin Kwankwaso da Obi’
Daga Muhammad Muhammad zahraddin
Dan takarar mataimakin shugaban kasa na jam’iyyar Labour Doyin Okupe, ya ce an kawo ƙarshen yunƙurin da ake yi na haɗewa tsakanin jam’iyyar Kwankwaso ta NNPP da ta Peter Obi wato LP.
Yayin wani shirin siyasa na kafar talabijin din Channels jiya Talata Mista Okupe ya ce tun kusan makwanni hudu da suka gabata aka kawo ƙarshen yunƙurin, amma sai ƴan jam’iyyar NNPP suka ci gaba da yaɗa arfaganda a kan batun dn ganin sun raɓa kansu da farin jinin da Mista Obi ke da shi a wajen yan Najeriya.
Ya ce Kwankwaso ya ki amincewa ya zama mataimakin shugaban ƙasa ga Obi ba tare da wani ƙwaƙƙwaran dalili da ya wuce saboda shi dan arewa ne ba.
”Ni na jagoranci ɓangarenmu na LP a wannan tattaunawa, daga lokacin da na nuna musu cewa yanzu lokaci ne da ya kamata a mika mulki ga yankin kudancin Najeriya amma suka ƙi amincewa muka nuna sasantawar ba za ta yiwu ba” in ji Mista Okupe.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
