News
Yanzu-Yanzu: Abba Kyari, Dariye, Nyame sun tsere daga magarkamar Kuje a wani hari
Daga Muhammad Muhammad zahraddin
Ana tunanin wasu manyan fitattun fursunoni a gidan yari na Kuje da ke babban birnin tarayya Abuja sun tsere a harin da wasu ‘yan bindiga suka kai a daren ranar Talata.
Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mataimakin kwamishinan ‘yan sanda, Abba Kyari da abokan harkallarsa da ke wurin, mai yiwuwa sun tsere daga magarkamar, a harin da ya dauki tsawon sa’o’i, an ce jami’an soji da masu gadin gidan yarin da ke bakin aiki sun yi artabu da tsagerun.
Legit.ng ta rawaito cewa, haka ma tsohon gwamnan jihar Filato Joshua Dariye da takwaransa na Taraba Jolly Nyame da majalisar kasa ta yi wa afuwa a baya-bayan nan.
Har yanzu gwamnatin tarayya ba ta aiwatar da sakin su Dariye ba har aka samu akasi aka kai hari magarkamar.
Majiyoyi a cikin magarkamar sun shaidawa jaridar The Nation cewa baya ga manyan fursunonin, wasu ‘yan ta’adda da sauran masu laifi sun tsere yayin da maharan ke luguden wuta.
Sai dai har zuwa lokacin da hada wannan rahoto, babu wani tabbaci a hukumance kan adadin wadanda suka tsere da bayanansu.
Karin bayani na nan tafe…
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
