News
An Sake Damke Fursunoni 551 Da Suka Tsere Daga Kurkukun Kuje
Daga Khadija Abdullahi Mahmud
An sake damke akalla mutum 551 daga cikin fursunoni 879 da suka tsere sakamakon harin da aka kai gidan gyaran hali na Kuje da k Babban Birnin Tarayya Abuja a Talatar da ta gabata.
Ya zuwa hada wannan labari, akwai ragowar fursunoni 328 da ake nema ruwa a jallo don a sake damke su.
Na ji takaici ga tsarin tsaron sirri na ƙasar nan -Buhari
Yayin harin, wasu mutum hudu daka cikin fursunonin da kuma jami’in NSCDC daya suka rasa ransu, yayin da mutum 16 suka ji rauni ana kuma ci gaba da yi musu magani.
Hukumar Kula da Gidajen Yari ta Kasa ta ce, ana ci gaba da kokarin ganin an sake kamo ragowar fursunonin da suka tsere baki daya.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
