Connect with us

News

Buhari ya ba ministan ilimin Najeriya umarnin kawo ƙarshen yajin aikin ASUU cikin mako biyu

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

 

 

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bayar da umarni ga ministan ilimi na ƙasar Malam Adamu Adamu da ya kawo ƙarshen yajin aikin malaman jami’o’in ƙasar.

 

Advertisement

Jaridar Daily Trust a Najeriya ta ruwaito cewa shugaban ya bayyana haka ne a ranar Talata inda ya bayar da umarni ga ministan ilimin ƙasar da ya sasanta abubuwan da ake taƙaddama a kai cikin mako biyu sa’annan a kai masa rahoto.

Kotu Ta Janye Umarnin Hana Ganduje Karbo Bashin N10bn

A yau Talata Shugaba Buharin ya tattauna da ma’aikatu da masu ruwa da tsaki waɗanda ke da alaƙa da ɓangaren ilimi a ƙasar da za su iya warware wannan tirka-tirkar.

 

Shugaban ya kira su ne domin ya samu ƙarin bayani kan dalilin da ya sa wannan yajin aikin ya ƙi ci ya ƙi cinyewa.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending