Connect with us

News

Gobara Ta Tashi A Makarantar Ma’aikatan A BUK A Kano

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAH 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Kano ta ce gobara ta kama tare da lalata wani sashe na Makarantar Firamaren Ma’aikatan Jami’ar Bayero ta Kano.

Advertisement

 

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da kakakin hukumar, Alhaji Saminu Abdullahi, ya fitar a ranar Laraba a Kano.

Advertisement

Mutum 189 Sun Kamu Da Kwalara A Kananan Hukumomi 20 A Kano

 

Advertisement

Ya ce gobarar ta tashi a makarantar ce da yammacin ranar Talata.

 

Advertisement

A cewar Abdullahi, “Mun samu kiran waya da misalin karfe 05:53 na yamma daga wani Halliru Bello, inda nan take muka aike da tawagarmu zuwa wurin da lamarin ya faru da misalin karfe 5:58 na yamma domin hana gobarar ta yadu zuwa wasu sassa na makarantar.

 

Advertisement

“Wani gini mai tsayi kafa 200 mai dauke da ofishin Shugaban Makarantar Firamaren da ofishin malamai maza da ofishin malamai mata da dakin ajiya da kuma bandaki sun kone a sanadin tashin gobarar.

 

Advertisement

“Ana binciken musabbabin tashin gobarar,” in ji shi.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending