News
Mutum 189 Sun Kamu Da Kwalara A Kananan Hukumomi 20 A Kano
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Akalla mutum 189 ne suka kamu da cutar amai da gudawa, wato Kwalara a kananan hukumomi 20 a Jihar Kano.
Kwamishinan Lafiya na jihar, Dokta Aminu Ibrahim Tsanyawa, ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Kano a ranar Talata.
ASUU ta magantu kan umarnin kawo ƙarshen yajin aikin da Buhari ya bayar
Ya ce, 184 daga cikin wadanda suka kamu da cutar sun warke, biyar sun mutu, kuma a yanzu jihar ba ta samu bullar cutar ba sakamakon hadin gwiwar jama’a daban-daban na jihar.
A cewarsa, Cibiyar Dakile Cututtuka ta Kasa (NCDC), ta samu mutum 2,339 da suka kamu da cutar ta Kwalara a cikin fiye da jihohi 30 daga watan Janairu zuwa Yunin 2022.
Ya kara da cewa har yanzu Najeriya na fama da cutar Kwalara musamman a lokacin damina saboda rashin tsaftar muhalli, rashin kula da shara a gida da kuma yin bayan gida a fili, wanda a cewarsa su ke taimakawa wajen yada kwayoyin cutar.
Kwamishinan ya bada tabbacin ci gaba da jajircewar gwamnati wajen samar da isassun kayan aiki na kiwon lafiya ga mutanen jihar domin kawar da barkewar cutar ta Kwalara da sauran cututtuka tare da yin kira ga jama’a da su tabbatar da tsaftar jikinsu da ta muhalli.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
