Connect with us

News

Gwamnatin Najeriya na duba yuwuwar hana hawa babur

Published

on

 

DAGA KHADIJA ABDULLAHI MAHMUD

 

 

 

Gwamnatin Najeriya ta ce tana duba yuwuwar hana amfani da babura domin dakile ayyukan masu satar mutane da ‘yan ta’adda.

Advertisement

 

Ministan Shari’a kuma babban lauyan gwamnati Abubakar Malami shi ne ya sanar da haka a karshen taron majalisar tsaron kasar wanda Shugaba Muhammadu Buhari ya jagoranta yau Alhamis a Abuja.

An sake maido da wutar lantarki a kasa Baki Daya bayan matsalar wutar da aka samu TCN

A jawabin nasa ga manema labarai, ministan wanda ke tare da takwaransa na ma’aikatar cikin gida Rauf Aregbesola da kuma na ma’aikatar kula da harkokin ‘yan sanda Alhaji Maigari Dingyadi, ya ce, gwamnati na tunanin hana amfani da baburan da kuma aikin hakar ma’adanai.

 

Ya ce za ta yi hakan ne domin dakile hanyoyin da ‘yan ta’adda da masu satar mutane ke samun kudade da kuma jigilar kayayyakinsu.

Advertisement

 

Ministan ya bayyana cewa amfani da baburan na bai wa ‘yan ta’adda damar jigilar kudade da suke samu daga aikin hakar ma’adanai, su sayi makamai.

 

Sai dai kuma Malamin bai bayyana inda dokar za ta shafa ba, walau kasar baki Daya ko kuma wani bangare na kasar.

 

Da yake nasa jawabin ministan cikin gida Aregbesola ya ce duk da irin tarin bayanan sirrin da aka yi kafin harin da aka kai kan gidan yari na Kuje ranar 5 ga watan nan na Yuli, ‘yan ta’adda sun samu nasara saboda babu kudurin yakar su, kamar yadda ya ce.

Advertisement

 

Ya kara da cewana baw a Shugaba Buhari rahoton farko-farko na binciken da aka yi kan harin, tari da alkawarin cewa duk jami’in da aka samu da sakaci a aikinsa za a hukunta shi.

 

 

BBC HAUSA

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending