News
Shafin Youtube ya amsa kiran Saudiyya, ya cire tallace-tallacen da suka saɓa wa Musulunci
DAGA MARYAM BASHIR MUSA
Shafin YouTube ya cire tallace-tallacen da hukumar kula da harkokin yada labarai ta Saudiyya ta yi Allah wadai da su da cewa sun saba wa kimar Musulunci ta kasar.
A wata sanarwa da shafin ya wallafa a shafinsa na Twitter, YouTube ya ce ba za a amince da tallace-tallacen ba, kuma ya dauki matakin gaggawa don dakatar da abin da ya kira masu cin zarafi da ke karya manufofin kamfanin.
CBN ta baiwa TajBank lasisin gudanar da harkoki a faɗin ƙasa
Matakin na zuwa ne kwanaki kadan bayan da kafafen yada labarai da hukumomin fasaha a Saudiyya suka yi gargadin cewa za a dauki matakan shari’a idan har YouTube bai dakatar da tallace-tallacen da ake gani a kasar ba.
Hakan ya biyo bayan wani kamfe da wasu ‘yan kasar Saudiyya suka yi ta Internet, inda suka koka kan yadda yara ke tallan da ba su dace ba a YouTube.
-
News2 days ago
Wani Matashi Mai Shekaru 18 Ya Rasa Ransa Bayan Fadawa Cikin Ruwa A Kano
-
News2 days ago
Kaduna, Nasarawa, Zamfara Da Wasu Jihohi 10 Na Fuskantar Barazanar Ambaliyar Ruwa —NiMet
-
News3 days ago
Ba Za Mu Yi Wa Kowa Rangwame Ba A Wajan Yaƙi Da Sha Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi Ba — Muhyi Magaji
