Connect with us

News

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta haramta aibata jami’anta a fina-finai

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Sifeta Janar na Yan sandan Najeriya ya gargadi masu shirya fina-finai a kasar da su guji aibanta aikin dan sanda a shirye-shiyensu na talabijin, ba tare da izinin rundunar ba.

 

Advertisement

IG Usman Baba ya kara da cewa daga yanzu ka da a ƙara ganin wani mutum sanye da kayan ɗan sanda a fina-finai, ba tare da izini ba kamar yadda doka ta tanadar.

 

Advertisement

Ya ce idan ba haka ba to kuwa duk wanda ya karya doka zai ɗanɗana kudarsa.

Ana zargin ‘yan-sintiri da kashe malamin makarantar allo a Jihar Kano

Advertisement

Masu shirya fina-finai a Najeriya kan kwaikwayi jami’an yan sandan kasar, kuma a mafi yawan lokuta ba a nuna su a mutanen kirki.

 

Advertisement

Sanarwar da rundunar yan sandan ta fitar ta ce “ka da wani mai shirya fina-finai da ya sake nuna ƴan sanda a matsayin marasa kirki ba tare da izini ba a rubuce daga rundunar yan sanda.”

 

Advertisement

Sanarwar ta ƙara da cewa ba za ta amince da bayyana aikin ɗan sanda ba a fina-finai, matsawar abin da aka kwaikwaya a aikin ba shi da kyakkyawan tasiri ga al’umma.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending