News
Kwamishinan matasa da wasanni na jahar yobe ya rasu
Daga Yasir sani Abdullahi
Goni Lawal, Kwamishinan Matasa da Wasanni na Jihar Yobe ya rasu.
Jaridar The Cable ta rawaito cewa Tijjani Ciroma, kakakin ma’aikatar ne ya tabbatar da hakan a yau Laraba.
Ya ce Lawal ya rasu ne a wani haɗarin mota da ya rutsa da su a hanyar Potiskum zuwa Azare da misalin karfe 7:30 na yammacin jiya Talata.
Ciroma ya ce marigayin, mai shekaru 57 a duniya yana kan hanyarsa ta zuwa Kano ne domin shiga jirgi zuwa Abuja domin gudanar da aikinsa.
Kakakin ya ce za a yi sallar jana’izar marigayin da misalin karfe 11 na safe a Cibiyar Musulunci ta Yobe da ke Damaturu.
An naɗa Lawal a matsayin Kwamishina a 2019.
Ya kasance mamba na majalisar wakilai
Kuma ya rasune a Wani asibiti dake dake potiskun a jahar ta yobe
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
