News
Yan sanda sun kama wanda ake nema ruwa a jallo, Rasheed Okoilu, a Osogbo
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Rundunar ‘yan sandan jihar Osun ta ce ta kama wani shahararren mai kisan gilla da ake nema ruwa a jallo, Rasheed Hamed, wanda aka fi sani da Rasheed Okoilu da sanyin safiyar Lahadi.
Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Osun, Yemisi Opalola ne ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da ya fitar a garin Osogbo, inda ya ce, rundunar ‘yan sanda ta hadin guiwa da jami’an ‘yan sanda daga ofishin ‘yan sanda na Dugbe da kuma ofishin ‘yan sanda na Oke Baale tare da goyon bayan mafarautan yankin sun cafke wanda ake zargin.
Ban taba bakin ciki ko nadama don an cire ni daga sarkin Kano ba — Sanusi II
Ms Opalola, Sufeto na ‘yan sanda, ta ce an bi diddigin wanda ake zargin tare da kama shi bayan da ya yi kisan kai a Egbatedo, Osogbo, inda ya kashe mutane uku.
Ta ce an mika wanda ake zargin ga sashin yaki da ayyukan asiri na rundunar ‘yan sanda a jihar kuma ana kan gudanar da bincike.
Kamfanin dillancin labarai na Najeriya ya tuna cewa, a ranar 10 ga watan Maris ne rundunar ‘yan sandan jihar Osun ta bayyana Rasheed Okoilu da wani Solomon Adedimeji (Solo Iwara) da ake nema ruwa a jallo bisa laifukan kisan kai, kone-kone, kashe-kashen al’ada, fashi da makami, fyade da kuma garkuwa da mutane.
Rundunar ‘yan sandan ta yi gargadin cewa duk wanda ya ajiye wadanda ake zargin za a dauke shi a matsayin wanda ke da hannu wajen aikata laifukan da suka aikata.
Sai dai rundunar ‘yan sandan ta yi alkawarin baiwa duk wanda ya samu bayanai masu amfani ga inda mutanen da ake nema suke, za su ba su kyauta mai kyau.
DAILY NIGERIAN
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
