News
A jira ni, zan bayyana matsayata cikin mako guda — Shekarau
Daga Muhammad Muhammad zahraddin
Tsohon gwamnan jihar Kano, Sanatan Kano ta tsakiya, Sardaunan Kano Malam Ibrahim Shekarau, yace rashin cika alkawarin da suka kulla kafin shigarsa jam’iyyar NNPP ya sanya magoya baya ke hasashen ficewa daga jam’iyyar.
Jawabin hakan ya fito ne daga bakin mai magana da yawun Shekarau, Dr. Sule Ya`u Sule, dukda cewa ya musanta rahoton da ake yadawa cewa zasu bar NNPP.
”A halin yanzu dai jama’a su yi watsi da duk wani labari a kan siyasar Malam Ibrahim Shekarau. A cikin makon nan da muke ciki za mu ba da cikakken bayani game da Siyasar Gidan Sanata Malam Ibrahim Shekara,” inji Dr. Sule Ya’u Sule
Sule yace an kafa kwamiti mai mutane talatin domin tattaunawa akan batun kafin yanke hukunci.
Sauran bayanai nanan tafe…
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
