Connect with us

Sports

Anthony Joshua ya sha kaye a hannun Usyk

Published

on

Joshua,

Daga: Usman Abdullahi jibirin

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

A jiya Asabar ne dai Anthony Joshua, ɗan dambe, wanda ya ke d5an kasar Birtaniya da Najeriya a birnin Jeddah na kasar Saudiyya ya zubar da hawaye bayan ya sha kaye a hannun Oleksandr Usyk, ɗan kasar Ukraine.

Usyk, a karawa ta biyu, ya doke Joshua ya kuma rike kambun IBO, IBF, WBA da WBO.

Advertisement

A taron manema labarai bayan fafatawar, Joshua ya zubar da hawaye, yayin da ya ke bayyana ɓacin ransa sakamakon kayen da ya sha a bayan fafatawar.

“Ba na jin komai, na damu sosai a cikin zuciyata, Lokacin da ka samu rashin nasara, ba za ka yi farin ciki ba, abin haushi ne kawai.

Advertisement

“Na so in yi nasara kuma na so in yi nasara sabo da ƴan Birtaniya saboda na san yadda suke so in fafata da Tyson Fury. Ban yi farin ciki da wasan nan ba saboda ban yi nasara ba.

“Na yaba da duk wadanda su ka kalli wasan nan a gida, ni mayaki ne, amma ba a cikin yanayi mai daɗi nake ba,” in ji shi.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending