Connect with us

News

Tankin ruwa ya kashe mutane 2 a Legas

Published

on

Daga Kabiru Basiru Fulatan

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa, NEMA, ta tabbatar da faɗowar tankin ruwa a kan mutane biyu har su ka rasa rayukansu a Ladi Lak, Bariga jihar Legas a daren jiya Lahadi.

Advertisement

Ibrahim Farinloye, Ko’odinetan shiyyar Kudu-maso-Yamma na NEMA, ya tabbatar wa Kamfanin Dillancin Labarai na Ƙasa, NAN faruwar lamarin a yau Litinin a Legas.

An samu karuwar yaduwar cutar kyandar biri a Najeriya

Advertisement

 

Farinloye ya ce tankin ya faɗo ne daga wani bene mai hawa biyu har ya faɗo a kan wasu maza su biyu, babba da yaro, yayin da wasu manya uku suka samu raunuka.

Advertisement

Ya ce shugabannin al’umma na yankin Bariga ne suka kai waɗanda suka jikkata asibiti kafin isowar jami’an agajin gaggawa.

Ya ce lamarin ya faru ne a titin Adeleye, Ladi Lak, Bariga, wani yanki na Legas.

Advertisement

 

 

Advertisement

Daily Nigerian

Error: Contact form not found.

Advertisements
Advertisements
Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending