News
Tankin ruwa ya kashe mutane 2 a Legas
Daga Kabiru Basiru Fulatan
Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa, NEMA, ta tabbatar da faɗowar tankin ruwa a kan mutane biyu har su ka rasa rayukansu a Ladi Lak, Bariga jihar Legas a daren jiya Lahadi.
Ibrahim Farinloye, Ko’odinetan shiyyar Kudu-maso-Yamma na NEMA, ya tabbatar wa Kamfanin Dillancin Labarai na Ƙasa, NAN faruwar lamarin a yau Litinin a Legas.
An samu karuwar yaduwar cutar kyandar biri a Najeriya
Farinloye ya ce tankin ya faɗo ne daga wani bene mai hawa biyu har ya faɗo a kan wasu maza su biyu, babba da yaro, yayin da wasu manya uku suka samu raunuka.
Ya ce shugabannin al’umma na yankin Bariga ne suka kai waɗanda suka jikkata asibiti kafin isowar jami’an agajin gaggawa.
Ya ce lamarin ya faru ne a titin Adeleye, Ladi Lak, Bariga, wani yanki na Legas.
Daily Nigerian
Error: Contact form not found.
