Connect with us

News

Atiku yayi watsi da bukatar Sule Lamido, ya tafi London rarrashin Wike

Published

on

Atiku

Daga: Muhammad Muhammad zahraddin

 

 

 

 

 

Advertisement

 

 

 

Bayan rahoton wata ganawa da akayi tsakanin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu tare da gwamnan jihar Rivers, Nyesom Ezenwo Wike, acan birnin London, tuni wasu rahotanni suka nuna cewa shima dan takarar PDP, Atiku Abubakar, ya bazama zuwa London domin rarrashin Wike akan mara masa baya don kaiwa gaci a babban zaɓen shekarar 2023.

Tun bayan gudanar da zaɓen fidda gwani na dan takarar shugaban kasa da jam’iyyar PDP ta gudanar, wanda Atiku yayi nasara, Wike yaja baya a sha’anin jam’iyyar, ya kuma gana da manyan jagororin siyasar Nigeria daga jam’iyyu daban-daban.

Hakan na zuwa ne a lokacin da tsohon gwamnan jihar Jigawa, Sule Lamido, ya bukaci jam’iyyarsu ta PDP ta kyale Wike yayi duk abinda zaiyi, domin a cewarsa bai isa ya hana Atiku samun nasara a jihar Rivers ba.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending