News
ASUU ta sake tsawaita yajin aikin jami’oi
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Ƙungiyar malaman jami’oi a Najeriya, ASUU ta yanke shawarar tsawaita yajin aikin da take gudanarwa.
Jaridar Punch ta rawaito cewa matakin ya zo ne bayan wata zazzafar tattaunawa da aka yi ranar Litinin game da yadda za a cimma matsaya tsakanin ƙungiyar da kuma gwamnati.
Jihohin Najeriya 10 ne suka fi wasu kasashen Afirka Girman GDP – Osinbajo
An ɗauki matakin ci gaba da yajin aikin bayan ganawar kwamitin zartarwa a hedikwatar ASUU da ke Jami’ar Abuja, babban birnin Najeriya.
Ƙungiyar ASUU dai ta shafe watanni tana gudanar da yajin aikin da ya tilastawa ɗaliban jami’oin gwamnati zama a gida.
ASUU na ganin gudanar da yajin aikin ne hanyar samun mafita ga tarin buƙatun da ta gabatar wa gwamnatin Najeriya ciki har da batun inganta musu albashi.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
