Connect with us

News

Ambaliyar ruwa na ci gaba da ɗaidaita Pakistan

Published

on

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Kudancin Pakistan na fuskantar barazanar karin ambaliyar ruwa a yayin da ruwa ke gangarowa daga kogin Indus wanda mamakon ruwan saman ya cika shi makil.

Advertisement

 

Fiye da mutane dubu daya da dari daya ne suka mutu sakamakon ambaliyar ruwan da ta shafi kaso daya bisa uku na kasar.

Advertisement

Breaking news EFCC ta kama kakakin majalisar Ogun a filin jirgin saman Legas

Wakiliyar BBC ta ce jami’ai a kasar sun ce mutune miliyan 1 da dubu dari biyu sun rasa muhallansu a gundumar Daadu, sannan sojoji na aikin kwashe wadanda ambaliyar ta shafa a yankin, yayin da kai kayan agaji yanki ke fuskantar tarnaki.

Advertisement

 

Tuni Majalisar Dinkin Duniya ta nemi tallafin dala miliyan 160 don taimaka wa mutane fiye da miliyan shida da suke matukar bukatar taimakon gaggawa ciki har da samar da tsaftataccen ruwan sha da abinci da kuma wuraren zama.

Advertisement

 

Tun bayan fara mamakon ruwan sama a watan Yuni, Pakistan ke fama da ruwan sama kamar da bakin kwarya wanda kasar ta jima bata ga irinsa ba.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending