News
Sojojin Najeriya sun kashe ‘yan fashin daji biyu a Kaduna
DAGA YASIR SANI ABDULLAH
Rundunar Sojin Najeriya mai yaki da ‘yan fashin daji a jihar Kaduna ta ce ta kashe wasu ‘yan fashin daji biyu a yankin Birnin Gwari, a kokarin da rundunar ke yi na fatattakar ‘yan fashin daga yankin.
Jaridar Daily Trust a Najeriya ta ambato Kwamishinan al’amuran cikin gida na jihar a wata sanarwa da ya fitar yana na cewa sojojin sun fara wani atisaye a yankunan Birnin Gwari da Sabon Layi da Kuringa, da Maganda, da Farin ruwa.
Breaking news EFCC ta kama kakakin majalisar Ogun a filin jirgin saman Legas
Ya kara da cewa ‘yan fashin dajin sun gamu da ajalinsu ne bayan da suka yi arangama da dakarun sojin Najeriya a garin Farin Ruwa.
Kwamishinan ya ce gwamnatin jihar Kaduna na yaba wa dakarun sojin game da samun nasara da suke yi a wannan atisaye a yankin.
