News
Na koma jam’iyyar ADP ne sabo da bata yi wa kowa laifi ba a Kano — Shaaban Sharada
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Tsohon hadimin Shugaban Ƙasa, Sha’aban Sharada ya ƙaddamar da takararsa ta gwamna a jam’iyyar ADP
Sha’aban Sharada ya ƙaddamar da takararsa ta gwamna a jam’iyyar ADP
Ɗan takarar gwamnan Kano a jam’iyyar ADP mai alamar littafi, Sha’aban Ibrahim Sharada, ya ce ya yanke shawarar sauya sheƙa zuwa jam’iyar ne sabo da bata yi wa kowa laifi ba a jihar.
2023: Sha’aban Sharada Zai Ayyana Neman Kujerar Gwamnan Kano a Yau
Sharada ya bayyana hakan ne a yayin da ya ke ƙaddamar da takararsa a hukumance a yau Asabar, a Sani Abacha Youth Centre a Kano.
Haka kuma ya ƙara da cewa, matuƙar ya kafa gwamnati a jihar Kano zai tabbatar da cewa, dukkan asibitocin jihar Kano sun samu wadatattu kuma ingantattun kayayyakin aikin lafiya.
A cewar sa, idan ya kafa gwamnati a Kano, zai samar da asibitoci na zamani a ɗaukacin mazaɓu 484 a ƙananan hukumomi 44 na jihar.
Sha’aban ya ƙara da cewa “Idan na kafa gwamnati zan tabbatar da cewa ƙananan hukumomi sun samu cikakken ƴancin cin gashin kai”.
Ya kuma yi alkawarin baiwa ƙananan hukumomi cin gashin kansu domin su ci gaba da yi wa al’umma ayyukan ci gaba don magance talauci.
Ya kuma kara da cewa a Kano babu wata jam’iyya mai farin jinin ADP, inda ya ce idan ta ci zaɓe to za ta saka wa al’umma da irin goyon bayan da su ke ba ta.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
