Connect with us

News

Na koma jam’iyyar ADP ne sabo da bata yi wa kowa laifi ba a Kano — Shaaban Sharada

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN

 

 

 

 

Tsohon hadimin Shugaban Ƙasa, Sha’aban Sharada ya ƙaddamar da takararsa ta gwamna a jam’iyyar ADP

Advertisement

Sha’aban Sharada ya ƙaddamar da takararsa ta gwamna a jam’iyyar ADP

 

 

Ɗan takarar gwamnan Kano a jam’iyyar ADP mai alamar littafi, Sha’aban Ibrahim Sharada, ya ce ya yanke shawarar sauya sheƙa zuwa jam’iyar ne sabo da bata yi wa kowa laifi ba a jihar.

2023: Sha’aban Sharada Zai Ayyana Neman Kujerar Gwamnan Kano a Yau

Sharada ya bayyana hakan ne a yayin da ya ke ƙaddamar da takararsa a hukumance a yau Asabar, a Sani Abacha Youth Centre a Kano.

Advertisement

 

Haka kuma ya ƙara da cewa, matuƙar ya kafa gwamnati a jihar Kano zai tabbatar da cewa, dukkan asibitocin jihar Kano sun samu wadatattu kuma ingantattun kayayyakin aikin lafiya.

 

A cewar sa, idan ya kafa gwamnati a Kano, zai samar da asibitoci na zamani a ɗaukacin mazaɓu 484 a ƙananan hukumomi 44 na jihar.

 

Sha’aban ya ƙara da cewa “Idan na kafa gwamnati zan tabbatar da cewa ƙananan hukumomi sun samu cikakken ƴancin cin gashin kai”.

Advertisement

 

Ya kuma yi alkawarin baiwa ƙananan hukumomi cin gashin kansu domin su ci gaba da yi wa al’umma ayyukan ci gaba don magance talauci.

 

Ya kuma kara da cewa a Kano babu wata jam’iyya mai farin jinin ADP, inda ya ce idan ta ci zaɓe to za ta saka wa al’umma da irin goyon bayan da su ke ba ta.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending