News
Wasu ‘Yan Siyasa Na Daukar Zaben 2023 Na Ko A Mutu, Ko A Yi Rai –INEC
DAGA MUSLIM YUNUS ABDULLAH
Hukumar zabe mai zaman kan ta ta kasa INEC, ta bayyana damuwar ta a kan yadda wasu ‘yan siyasa ke daukar zaben shekara ta 2023 a matsayin na ko a mutu ko a yi rai.
Jami’an hulda da jama’a na hukumar Festus Okoye ya bayyana haka a Abuja, yayin kaddamar da tawagar tattauna rikicin zabe da cibiyar bankasa harkokin dimokuradiyya CDD ta shirya.
Nasa ta sake soke ƙudirin harba gagarumin kumbo zuwa duniyar wata karo na biyu cikin mako ɗaya
Ya ce hukumar zabe ta na jin dadin yadda ‘yan jarida ke watsa labarum ta, amma ya dace a rika samun sahihan labarai daga gare ta ta hanyar tuntubar ta.
Festus Okoye, ya ce Hukumar zabe ta na da kyakkyawar alaka tsakanin ta da ‘yan jarida wajen bayyana wa al’umma labarun ta, amma ana samun labarun karya da ake yada wa mutane.
Ya ce kamar yadda su ke samun karuwar labarun karya da ake jingina wa hukumar, sun dauki matakin yaki da lamarin ta hanyar tsaftace labarun harkokin siyasa musamman ga wadanda su ka tsaya takara.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
