News
Obasanjo Yace Ya Yi Nadamar Goyon Bayan Buhari A 2015
DAGA YASIR SANI ABDULLAH
Tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo, ya ce ya yi nadamar goyon bayan shugaba Muhammadu Buhari a shekara ta 2015.
Obasanjo ya bayyana haka ne, yayin hirar sa da wata marubuciya Ifedayo Agoro a jirgin sama, wadda ta wallafa a shafin ta na Twitter, inda ta ce ta hadu da Obasanjo a baya-bayan nan kuma ta zauna kusa da shi a jirgin sama.
Yadda Ta Kaya A Manyan Wasannin Firimiyar Ingila Ranar Asabar
Miss Agoro Ta ambato Obasanjon ya na cewa, na yi babban kuskure wajen goyon bayan shugaba Buhari, domin bai san komai game da tattalin arziki ba.
Obasanjo, ya ce babban kuskuren da su ka yi shi ne, sun yi tunanin shugaba Buhari zai yi yaki da cin hanci da rashawa da rashin tsaro, sannan ya zabi mutanen da su ka san tattalin arziki da ayyuka.
Tsohon shugaban kasar, ya kuma zargi matasan Nijeriya da rashin hadin kai wajen yakar tsofaffin ‘yan siyasa, ya na mai cewa, idan matasa ba su tashi da gaske sun canza shugabancin Nijeriya ba babu abin da zai sauya.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
