News
Osinbajo ya sauka a Nairobi domin bikin rantsar da sabon shugaban ƙasar Kenya, Ruto
DAGA KAN BASIRU FULATAN
Mataimakin shugaban ƙasa, Farfesa Yemi Osinbajo, ya sauka a Nairobi babban birnin ƙasar Kenya domin halartar bikin rantsar da sabon Shugaban kasar William Ruto.
Mataimakin shugaban ƙasan dai ya sauka ne a filin jiragin sama na Jomo Kenyatta, inda ya samu tarbar tsohon gwamnan yankin Kwale, Salim Mvurya da jakadan Najeriya a ƙasar, Yusuf Yumusa da sauran manyan jami’an gwamnati.
Nayi yunkurin kashe mahaifina ne don in samu gado in sayi babur – Nasir Kabir
Tun a ranar 15 ga watan jiya na Agusta ne hukumar zaben ƙasar ta Kenya ta sanar da sunan mataimakin shugaban ƙasar, Ruto a matsayin wanda ya lashe zaɓen shugaban ƙasar, wanda aka yi a ranar 9 ga watan na Agusta.
Haka kuma ta ƙara da cewa, Farfesa Yemi Osinbajo ya samu rakiyar karamin ministan harkokin waje, Ambasada Zubairu Dada da mai bai wa shugaban ƙasa shawara akan harkokin siyasa, Sanata Babafemi Ojudu.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
