Connect with us

News

TIRƘASHI: Kansila ya naɗa muƙamai 32 a Kaduna

Published

on

Abubakar Sadiq
Advertisements
ads

DAGA MUSLIM YUNUS ABDULLAHI 

 

 

 

 

 

Advertisement

 

 

 

 

 

Abubakar Sadiq, Kansila mai wakiltar mazaɓar Saminaka a Ƙaramar Hukumar Lere a Jihar Kaduna, ya naɗa masu bashi shawara har guda 32.

Advertisement

 

Tuni dai takarda mai ɗauke da sunayen masu riƙe da mukaman da kuma ɓangarorin da za su jagoranta ta karaɗe kafofin sadarwa na zamani.

Ruwan Sama Da Kankara Ya Lalata Gonaki 300 A Katsina

Sai dai kuma da ya ke zanta wa da jaridar DAILY NIGERIAN, Kansilan ya ce ya naɗa waɗannan ɗumbin muƙamai ne domin ya rama alheri da alheri.

 

A cewar sa, duk waɗanda ya naɗa ɗin, su ne su ka tsaya tsayin-daka har sai da ya samu nasara, shi ya sa shima ya saka musu da irin soyayyar da su ke nuna masa.

Advertisement

 

Sadiq, wanda shine shugaban masu rinjaye na majalisar Ƙaramar Hukumar, ya ce biyan waɗannan ɗumbin ma’aikata nasa ba abu ba ne mai wahala domin tuni ya tanadi albashinsu da walwalarsu.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending