Connect with us

News

An Kashe ’Yan Bindiga Suna Tsaka Da Rabon Kudin Fansa

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAH 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

An kashe wasu masu garkuwa da mutane a yayin da suke tsaka da rabon kudin fansa a maboyarsu a cikin daji.

 

Advertisement

Jami’an tsaro sun aika ’yan bindigar lahira ne a musayar wuta a wani daji a Karamar Hukumar Moro ta Jihar Kwara, ranar Talata da dare.

 

Advertisement

Na Yafewa Duk Masu Zagina -Tahir I Fagge.

An ritsa bata-garin ne a maboyarsu, suna cikin raba kudin fansar matar da dan dan takarar Majalisar Dokokin Jihar Kwara a Jam’iyyar APC, Honorabul Lawal Ayansola Saliu, wanda aka fi sani da LAS.

Advertisement

 

Kakakin ’yan sandan Jihar Kwara, Ajayi Okasanmi, ya ce, “’Yan sanda da ’yan banga da mafarauta ne suka ritsa bata-garin suna tsaka da rabon kudin da suka karba daga iyalan mutanen da suka sace.

Advertisement

 

“Bata-garin sun bude wa jam’ian tsaron wuta, inda a yayin musayar wuta aka kashe biyu daga cikinsu, kamar yadda likitoci suka tabbatar bayan an kai su Asibitin Koyarwa na Jami’ar Ilori (UITH).”

Advertisement

 

Okasanmi ya ce an kwace wata mota kirar Honda Accord da wata bindiga daga hannun masu garkuwa da mutanen.

Advertisement

 

Ya kara da cewa ana bin sawun ragowar da suka tsere domin su girbi abin da suka shuka.

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

DAILY TRUST

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending