Business
Najeriya da Morocco sun sanya hannu kan yarjejeniyar shimfida bututun iskar gas
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Kasashen Morocco da Najeriya sun rattaba hannu kan yarjejeniyar da za ta bayar da damar shimfida bututun iskar gas daga Najeriya zuwa Morocco.
Aikin na tsawon kilomita 7,000 zai hade da bututun arewacin Afirka da ke tura gas zuwa kasashen Turai wanda ke arewacin Morocco.
Sabon Ginin Beni Da Ake Ginawa Shima Ya Fara Rikitowa A Kano
Shugaban kamfanin mai na Najeriya Mele Kyari ya shaida wa maharta taron sanya hannun wanda aka yi a birnin Rabat na kasar Morocco cewa aikin zai inganta walwalar jama’a tare da magance matsalar hamada da ake fuskanta a wasu yankunan yammacin Afirka.
A watan da ya gabata ne kasar Algeriya ta daina amfani da bututun da ke bi ta Morocco zuwa Spain, abin da ya janyo wa Moroccon koma-baya ta fuskar man gas da kudin fito da kasar ke karba.
A sanarwar da kamfanin na NNPC ya fitar ya ce aikin zai samar wa kasashen yammcin Afirka kudaden shiga ta hanyar karbar kudin fito na gas din da ke bi ta kasashensu.
Kawo yanzu dai ba a san yaushe aikin zai kammala ba, wanda ake sa ran fitar da gas mai tarin yawa a kowacce rana.
BBC NEWS
-
News2 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
