News
ASUU: Gwamnatin Kaduna ta gargadi kungiyar daliban Najeriya kan rufe hanyar Kaduna-Abuja
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Gwamnatin jihar Kaduna da ke Najeriya ta gargadi Kungiyar dalibai ta kasar da kada ta toshe hanyar Kaduna zuwa Abuja kamar yadda ta shirya.
Kwamishinan Tsaro da Lamuran Cikin Gida, Samuel Aruwan, ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar.
Ya ce “ba za mu amince da matakin daliban ba, don karya doka da oda ne.”
Sanarwar ta kara da cewa lamarin ka iya haifar da tashin hankali don haka ta gargadi ‘yan jihar da kada su sa kansu a cikinsa.
Rahotanni sun nuna cewa daliban na nuna fushinsu ne kan watanni bakwai da aka shafe ana yajin aikin malaman jami’o’i, wanda hakan ya sa kungiyar daliban ta yanke hukunci datse manyan hanyoyin sufuri, ciki hadda titin da ya tashi daga Kaduna zuwa Abuja, da kuma filin jirgin saman Nnamdi Azikwe da ke Abuja har sai an biya musu bukatunsu.
Ko a ranar Litinin sai da daliban su ka toshe hanyar da ke zuwa filin jirgin Murtala Muhammad da ke Legas, lamarin da ya haifar da rudani da soke tashin wasu jiragen sama, kasancewar fasinjoji sun shafe sama da awa takwas a cunkoson motoci.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
