News
Kotu ta umarci ASUU ta koma bakin aiki
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Kotun Ma’aikata ta Kasa ta umarci kungiyar malaman jami’o’i ta janye yajin aikin da take yi.
Da yake gabatar da hukunci kan bukatar wucin gadi da gwamnatin tarayya ta nema, Mai shari’ah Polycarp Hamman ya hana kungiyar ASUU ci gaba da yajin aiki har zuwa lokacin yanke hukunci kan shari’ar.
ASUU: Gwamnatin Kaduna ta gargadi kungiyar daliban Najeriya kan rufe hanyar Kaduna-Abuja
A farkon watan nan ne gwamnatin ta gurfanar da ASUU a gaban kotun kan yajin aikin da ta kwashe wata bakwai tana yi.
Mai shari’ah Polycap Hamman, wanda alkali ne da ke sauraron shari’ah a lokacin da kotun ke hutu ya kuma mayar da karar zuwa ga shugaban kotun ma’aikata don ya sake bai wa wani alkali wannan shari’ah. Ma’aikatar kwadago ta kasar ta ce gwamnati ta dauki mataki ne bayan tattaunawa da kungiyar malaman jami’o’in ta ci tura. A zamanta na farko, kotun karkashin jagorancin mai shari’a, Polycarp Hamman ta dage sauraren karar zuwa yau Laraba bayan ta saurari bayanai daga wurin masu shigar da kara da wadanda aka shigar kara. Gwamnatin tarayya tana son kotun ta bayyana halarci ko haramcin yajin aikin na ASUU.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
