Business
Afirka ta Kudu ta gargadi MTN kan yaudarar masu sayen datar kwana 1
DAGA MUSLIM YUNUS ABDULLAH
Hukuma ta gargadi kamfanin wayar salula mafi girma a Afirka saboda yaudarar abokan huldarsa game da sayar musu da kunshin data na kwana 1.
A yanzu kunshin datar MTN ta kwana 1 ba ta karewa bayan awa 24, maimakon haka tana karewa ne cikin tsakar daren ranar da mutum ya sayi datar, ba tare da la’akari da komai kurewar lokacin da aka saya ba.
Ofishin kula da Harkokin Tallace-tallace na Afirka ta Kudu ya bayyana shirin a matsayin “mai fuska biyu don haka akwai yaudara a cikinsa”, abin da ya sa hukumar ta nemi MTN a wannan mako ya janye tallace-tallacen da yake yi na kunshin datar.
Wata kafar yada labarai mai suna Business Insider South Africa ce ta yada hoton tallar kunshin datar na MTN, lamarin da ya haifar da korafe-korafe.
BBC
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
