Connect with us

News

Ahmed Lawan ya karbi kaddara kan hukuncin kotun da ya soke takararsa

Published

on

Ahamed lawan

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI

Shugaban Majalisar Dattijai Sanata Ahmed Lawan ya ce ya karbi hukuncin Babbar Kotun Tarayya da ya ce ba shi ne halattaccen dan takarar majalisar dattijai na jam’iyyar APC a mazabar Yobe ta Arewa ba.

Advertisement

Matakin na zuwa ne kwana guda bayan hukuncin kotun da ke zamanta a birnin Damaturu game da halattaccen dan takarar sanata a jam’iyyar APC daga mazabar Yobe ta Arewa.

Cikin sanarwar da ya wallafa a shafinsa nasada zumunta, Sanata Ahmed Lawan ya ce bayan tuntubar abokan harkar siyasa da magoya baya da abokan arziki, “Na yanke shawara ba zan daukaka kara a kan hukuncin ba. Na karbi kaddara”.

Advertisement

Sanarwar ta kunshi wani bayani mai alamta yin ban kwana, inda ya yi godiya ga shugabannin siyasar jiharsa ta Yobe da ma al’ummar mazabarsa da ya wakilta tsawon shekaru a majalisun tarayyar Najeriya.

BBC

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending