News
Kashi 60 na daliban da rubuta NECO ne suka ci jarrabawa
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Dalibai sama da 700,000 ne suka ci jarrabawar kammala sakandire ta 2022 wadda Hukumar Tsara Jarrabawa ta Kasa NECO.
Gidan talbijin na Channels ya ruwaito, Babban Jami’in Hukumar, Farfesa Ibrahim Dantani Wushishi lokacin da yake sanar da haka a wani taron manema labarai a Minna.
Ya ce masu ruwa da tsaki da dama sun tantance cewa an samu gagarumar nasara a jarrabawar kammala sakandire da hukumar ta yi a shekarun baya-bayan nan.
Wushishi ya ce a cikin dalibi 1,198,412 da suka rubuta jarrabawar, dalibi 727,864 wato kashi 60.74 ne suka ci jarrabawar da fiye da darasi biyar ciki har da Ingilishi da Lissafi.
Farfesa Ibrahim Wushishi ya shawarci
daliban da suka rubuta jarrabawar su duba shafin hukumar NECO don ganin sakamako.
BBC
-
Opinion4 days ago
Ayyuka, Bin Diddigi, Biyan Kudi, Sakamako: Dabarun Kano Da Suka Zarce Jihohi 35
-
Opinion4 days ago
Tiriliyan ₦210 na Karya: Yadda Bala Wunti Ya Warware Dukkan Rudanin da Ya Mamaye Zaman Majalisar Dattawa Kan Asusun NNPC
-
News4 days ago
Jihar Kano Ta Shiga Jerin Jahohi 10 Mafi Tara Kudaden Shiga Na VAT A 2026
