News
Ginin coci ya danne mutane da dama a Anambra
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Ana fargabar mutane da dama sun maƙale a ƙarƙashin ɓaraguzan ginin wani coci da ya rushe a jihar Anambra da ke kudu maso gabashin Najeriya.
Lamarin ya faru ne a jiya Lahadi a Cocin Katolika na Madonna Catholic a Iyiowa, da ke yankin Odekpe a ƙaramar hukumar Ogbaru, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.
Wani ɗan majalisar dokokin Katsina ya rasu a Saudiyya
Yankin na daga cikin yankunan jihar da dama da ke fama da ambaliyar ruwa da ake zaton ita ta jawo rushewar ginin.
Har yanzu ba a san adadin yawan wadanda lamarin ya rutsa da su ba yayin da ake ci gaba da aikin ceto a wajen.
Advertisements
