News
Za mu janye yajin aiki nan ba da jimawa ba – ASUU
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Shugaban kungiyar malaman jami’o’i ta Najeriya, ASUU, Farfesa Victor Emmanuel Osodekeya ce nan ba da jimawa za su koma azuzuwa domin ci gaba da koyarwa.
Ƴan Nijeriya sun kashe dala miliyan 609.5 wajen karatu a ƙasashen waje a wata 8
Ya bayyana haka ne yayin da ya gana da kakakin majalisar wakilan Najeriya, Femi Gbajabiamila ranar Litinin.
Farfesa Osodeke ya yaba wa matakin da majalisar wakilan kasar ta dauka na shiga tsoma baki domin ganin an yi sulhu tsakanin gwamnatin tarayya da kungiyar ASUU wadda ta kwashe wata takwas tana yajin aiki.
Wani bidiyo da aka wallafa a shafin Tuwita na majalisar wakilan Najeriya ya nuna Farfesa Osodeke yana cewa sun kusa kawo karshen yajin aikin.
BBC
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
