Connect with us

News

Yan Bindiga Sun Kai Hari Sakatariyar Karamar Hukuma A Ebonyi

Published

on

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADEEN 

 

 

 

 

 

Advertisement

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Ebonyi ta ce, wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wane ne ba sun kai hari Sakatariyar Karamar Hukumar Ezza ta Arewa a jihar a ranar Litinin.

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ya rawaito cewa, maharan sun banka wa ginin sakatariyar wuta tare da lalata muhimman abubuwa na miliyoyin Naira.

Ƴan Nijeriya sun kashe dala miliyan 609.5 wajen karatu a ƙasashen waje a wata 8

Mai magana da yawun rundunar, SP Chris Anyanwu, ya tabbatar da aukuwar lamarin ga NAN.

Ya kara da cewa ba su kai ga tattara cikakken bayani game da harin ba, amma suna kan gudanar da bincike domin gano masu hannu a cikinsa.

Sa’ilin da yake yi wa manema labarai karin haske dangane da harin, Shugaban Karamar Hukumar, Mista Ogodo Nomeh, ya ce an yi dauki-ba-dadi tsakanin jami’an tsaro da maharan.

Advertisement

Sannan kawo yanzu babu wanda aka kama dangane da harin.

 

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending