Connect with us

News

Wani magidanci ya kashe matarsa ta hanyar lakada mata duka a Ogun Police

Published

on

Police

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN

 

 

 

 

 

Advertisement

 

 

 

 

 

 

Advertisement

‘Yan sandan Jihar Ogun sun kama wani mutumi mai shekara 51, mai suna Oluranti Badejo, saboda zargin kashe matarsa, Folasade Badejo, bayan lakada mata duka.

Jaridar Daily Trust a Najeriya ta ruwaito cewa lamarin ya faru ne a garin Orimerunmu, Mowe da ke karamar hukumar Obafemi-Owode na jihar ta Ogun.

Kotu Ta Saki Shugaban IPOB Nnamdi Kanu

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, Abimbola Oyeyemi, ya fadawa manema labarai cewa an kama wanda ake zargin ne bayan kai musu rahoto da kanwar marigayiyar ta yi.

A cewar Abimbola, kanwar mamaciyar ta fada musu cewa ‘yar karamar sabani ne ta shiga tsakaninsu da kuma ya kai ga mijin lakadawa matarsa duka har ya yi sanadiyyar mutuwarta.

“A lokacin da ya gano cewa matarsa ta mutu, ya yi amfani da dutsen guga wajen kona wasu sassan jikin marigayiyar saboda a ce wutan lantarki ne ya kasheta, sai dai, bai san cewa karamar ‘yar su mai shekara takwas na kallonsa lokacin da yake aikata hakan,” in ji Oyeyemi.

Advertisement

A yanzu dai ana tsare da wanda ake zargin a sashen masu aikata laifin kisa na rundunar ‘yan sanda jihar ta Ogun, inda ake ci gaba da bincike

 

 

 

BBC

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending