Connect with us

News

An katse intanet a Sudan

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN

 

 

Advertisement

An katse intanet a kasar Sudan a yayin da ake shirin bikin zagayowar cika shekara daya da gudanar juyin mulkin soja.

Ana gudanar da zanga-zanga kusan duk mako a kasar tun bayan da Janar Abdel Fattah al-Burhan ya kwace mulki hannun farar hula.

Advertisement

Putin zai kai karar Ukraine Majalisar Dinkin Duniya

An kashe akalla mutum 118 tun da aka soma zanga-zangar a watan Oktoban bara.

Advertisement

Masu rajin kare demokradiyya sun yi kira a gudanar da zanga-zanga a manyan birane da garuruwa a kasar.

A Khartoum babban birnin kasar masu rajin kare hakkin dan adam na shirin yin maci zuwa fadar shugaban kasar.

Advertisement

Tun bayan da aka hambarar da gwamnatin Omar al-Bashir a shekara ta 2019, sojojin sun yi alkawarin mika mulki ga farar amma har yanzu suna ta jan kafa.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending