Connect with us

Sports

Pogba Ba Zai Buga Gasar Cin Kofin Duniya Ba

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Dan wasan tsakiyar Juventus kuma dan kasar Faransa, Paul Pogba ba zai buga Gasar Cin Kofin Duniya ba da za a yi a kasar Qatar, sakamakon rauni da yake fama da shi.

Advertisement

 

Wakilin dan wasan Rafaela Pimenta ne ya bayyana haka ga manema labarai a yammacin ranar Litinin.

Advertisement

 

Mai Martaba Sarkin Dosso ya rasu yana da shekara 99

Advertisement

Pogba na fama da ciwo a gwiwarsa, lamarin da ya hana shi tabuka abun a-zo-a-gani tun bayan raba gari da kungiyarsa ta Manchester United.

 

Advertisement

Dan wasan ya taka muhimmiyar rawa wajen taimaka wa Faransa ta lashe Gasar Kofin Duniya a shekara hudu da suka wuce.

 

Advertisement

Pogba ya bar kungiyar kwallon kafa ta Manchester United, watanni shida da suka wuce, sai dai ya gaza taimaka wa kungiyar ta Juventus da ke fama a gasar Seria A, sakamakon rauni da yake fama da shi.

 

Advertisement

Dan wasan dai ya rattaba wa Juventus hannu kan kwantaragin shekara hudu a karo na biyu.

 

Advertisement

Mai shekara 29 a duniya, ya buga wa kungiyarsa wasanni biyu ne kacal sakamakon raunin da ya samu, bayan sake dawowarsa kungiyar a karo na biyu.

 

Advertisement

Wannan ta sa ba zai sami damar wakiltar kasarsa ba a Gasar Cin Kofin Duniyar da za a fara a ranar 20 ga watan Nuwamba, 2022, a kasar Qatar.

 

Advertisement

 

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending